Wani balaraben kauye ya zo wajen manzon Allah (ﷺ). Ya ce " ya rasulillah ﷺ idan na tashi roƙon Allah mai zan roƙa?". Sai manzon Allah ﷺ ya ce ma sa, " ka roƙe shi lafiya",. Sai wannan balaraben ya ƙara tambayar sa, mai zan roƙa? Sai manzon Allah sallallahu alaihi wasallam ya ƙara ce masa ka roƙe shi lafiya, sai da su kai haka sau uku yana tambayar sa manzon Allah sallallahu alaihi wasallam ya na ce masa ka roƙe shi lafiya.
Ya hayyu ya qayyum dan girman kaunar da ka ke yiwa fiyayyen halitta manzon Allah sallallahu alaihi wasallam Allah ka rawa A A ZAURA lafiya amin ya hayyu ya qayyum