@yusen0x: Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) ya shawarci gwamnatin Najeriya da ta yi la’akari da ƙaƙaba ƙarin haraji kan kayayyakin man fetur da kuma ayyukan sadarwa domin ƙara kuɗaɗen shiga. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan Najeriya ke kokawa da tsadar rayuwa, hauhawar farashi da ƙarin kuɗin sadarwa. Shin ƙarin haraji ne mafita ga matsalar tattalin arziki, ko kuwa zai ƙara jefa talakawa cikin wahala?