@tukur.garba.kakando: Daya daga cikin limaman Babban Masallacin Kasa da ke Abuja, Farfesa Ibrahim Maƙari, ya bayyana cewa ya cire rai kan shugabannin Najeriya wajen kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro da ke addabar ƙasar. Farfesa Maƙari ya bayyana hakan ne a cikin wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, inda ya nuna matuƙar damuwarsa kan yadda matsalar tsaro ke ci gaba da ta’azzara a sassa daban-daban na Najeriya. Ya ce duk da irin ƙoƙarin da ake ikirarin ana yi, har yanzu hare-haren ‘yan bindiga, sace-sacen mutane domin neman kuɗin fansa da sauran ayyukan ta’addanci na ci gaba da jefa al’umma cikin fargaba da rashin tabbas. Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.