@expressradionigeria: “Duk mutumin da aka ba shi takara a Kwankwasiyya, ina ba shi shawara ya riƙe kuɗinsa. Idan gudunmawa aka ba shi, ya riƙe gudunmawarsa. Idan kuma kai mai ba da gudunmawa ne, kada ka sake ka zuba, domin ba za su dawo ba. Kwankwasiyya an gina ta ne bisa amana, amma yanzu duk wanda yake da hankali ya san yadda aka tsayar da ’yan takara, babu maganar amana a cikinta. Babu wanda nake tausaya wa yanzu a cikinta yadda ake walagigi da shi kamar Jagora Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.” — Malam Ali Muhammad Bichi, Mai Bai wa Gwamnan Kano Shawara kan Yaɗa Farfaganda Mai Ma’ana. #ExpressRadioNigeria #Kwankwasiyya #Kano #NNPP