@trtafrikaha: 'Yan Nijeriya sun shiga ruɗani da mamaki gami da laluben amsoshi bayan fitowar bayanai kan wata badaƙalar kafa hukumar bogi a ƙarƙashin Ofishin Shugaban Nijeriya. Lamarin ya ɗaure kan jama'a ne bayan Fadar Shugaban Ƙasar ta fitar da wata sanarwa tana bayani kan yadda wani mai suna Adeneyi Adeyemi Matthew ya kafa wata hukumar gwamnati ta bogi, har ma yake mu'amala da halastattun hukumomin gwamnati da ma jakadun ƙasashen waje. Ko da yake wanda ake zargi ɗin ya ce hukumarsa ba ta bogi ba ce, kuma gwamnati ce ta kafa hukumar ta naɗa shi shugabanci.