@zayyanuasale: Mai Girma Gwamnan Jihar Neja, Manomi Umaru Mohammed Bago, ya gudanar da taron ruwa da tsaki tare da shugabanni da jagororin ƙananan hukumomin Mariga da Mashegu, inda suka yi zama da shugabannin tsaro domin lalubo hanyoyin magance matsalolin rashin tsaro da suka addabi yankunan. Allah Ya kawo mana ƙarshen wannan matsala, Ya ba mu zaman lafiya, lafiya da kwanciyar hankali a yankunanmu da ƙasarmu baki ɗaya. Ameen.