@journalists60: Nasarar da Sifaniya ta samu a kan Argentina da ci 1-0 a wasan ƙarshe na Gasar Kofin Duniya ta fito da yadda siyasa da rikicin yankin Gabas ta Tsakiya suka jawo wa ƙasar Argentina bakin jini a kokarin ƙasar na sake cin babban kofin a karo na huɗu a tarihi. Tun gabanin wasan wanda aka buga a ƙarshen mako, kan wasu daga cikin masu sha’awar ƙwallon ƙafa a duniya ya rabu biyu yayin da wasu suke goyon bayan Argentina, wasu suna goyon bayan kasar Sifaniya ne. A cikin wannan bidiyon mun yi duba kan yadda batun Falasɗinu da Isra'ila ya yi tasiri wajen sa ƙasashen Musulmai suka goyi bayan Sifaniya a wasan na ƙarshe.