@trtafrikaha: Shugaban Nijeriya Bola Tibnubu ya yi kira ga gwamnonin ƙasar su fi mayar da hankali wajen gina hanyoyin da za su inganta rayuwar jama'a da tsaro, maimakon gina gadojin sama a wuraren da ba a buƙatarsu. Tinubu ya yi wannan kira ne a fadar gwamnati a Abuja, lokacin da sarakunan gargajiya daga Jihar Oyo suka kai masa ziyara ƙarƙashin jagorancin Shugaban Sarakunan Ƙasar Ibadan wato Olubadan of Ibadanland Oba Rashidi Adewolu Ladoja a ranar Alhamsi. Shugaban ya yi kira ga basaraken wanda shi ma tsohon gwamna ne da ya taimaka wajen isar da wannan saƙo ga gwamnonin. Tinubu ya kuma bayyana cewa kuɗin da yake bai wa johihi a yanzu ya ninka abin da suke samu a baya sau biyar, inda ya ce a yanzu babu wata jiha da take cin bashi don biyan albashi.