@dokinkarfetv: BABBAR MAGANA: Cikin Minti Biyu Tinubu Ya Jefa Najeriya A Masifar Da Har Yau Ba Ta Fita Ba A Ranar Da Aka Rantsar Da Shi, In Ji Sadiq Sani Sadiq Jarumi a masana'antar Kannywood, Sadiq Sani Sadiq ya bayyana cewa tun a tashin farko Tinubu ya jefa ƴan Najeriya cikin bala'i ta hanyar cire tallafin man fetur a ranar da aka rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasa a shekarar 2023. Sadiq, ya bayyana hakan ne a cikin shirin Podcast na Dokin Ƙarfe TV, inda ya ƙara da cewa: "Tun kan a gama rantsar da shi farashin Dala ya ɗaga aka kuma fara haɗa layin mai a gidajen mai; masifar da har yau talakan Najeriya ke ciki kenan". In ji shi. Ku dakace mu nan gaba kaɗan domin samun cikakkiyar tattanawar. #nigeriantiktok🇳🇬 #hausatiktok #kano #dokinkarfetv #africa