@fagge_media: Wasu ƙungiyoyin mata a Jihar Kaduna sun fara wani gangami na wayar da kan mata kan muhimmancin ƙin karɓar kuɗi ko kayan masarufi domin sayen ra’ayinsu kafin zaɓe. Ƙungiyoyin sun kuma yi kira da a ƙara haɗin kai da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai daban-daban a Jihar Kaduna, domin gina al’umma da za ta iya rayuwa cikin fahimtar juna. Hajiya A’ishatu Gambo, ɗaya daga cikin shugabannin ƙungiyoyin da suka shirya gangamin, ta bayyana muhimmancin wayar da kan mata kan rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaɓe mai inganci. Fagge Media Agency | Muryar Gaskiya A ganinku, ya kamata ɗan ƙasa ya karɓi kuɗi ko kayan masarufi kafin zaɓe, ko kuwa hakan na iya shafar yadda zai zaɓa? #DuniyarLabarai #FaggeMediaAgency #MuryarGaskiya #Kaduna #KadunaState