@salaahamedia_tv: Shugaba Tinubu Ya Kawo ƙarshen Talauci A Fannin Ilimi A Najeriya babu talakan da bai zuwa makaranta sabo da talauci — Minista Ministar Ƙaramar Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad, ta ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kawo ƙarshen matsalar da ke hana ‘ya’yan talakawa samun ilimi a Najeriya. Ministar ta bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta samar da rancen karatu, tallafin makaranta da kuma shirye-shiryen horas da matasa sana’o’i domin tabbatar da cewa babu ɗalibin da zai bar karatu saboda rashin kuɗi. Ta ce a ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, gwamnati na ƙoƙarin bai wa matasa damar samun ilimi da ƙwarewar dogaro da kai, domin rage zaman banza da talauci a ƙasar nan. Sai dai furucin na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke kokawa kan tsadar rayuwa da wahalar tattalin arziki, lamarin da ya sa mutane da dama ke ganin har yanzu talauci na ci gaba da hana wasu yara zuwa makaranta.